Dandalin Siyasa - Shugaba Buhari ya lashe zaben Najeriya wa'adi na biyu
Listen now
Description
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne game da nasarar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu ta sake lashe kujerar shugabancin kasar wa'adi na biyu bayan doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar. Tuni Jam'iyyar PDP ta bayyana sakamakon zaben a matsayin mara inganci tana mai zargin tafka magudi a zaben,yayinda ta ce, za ta shigar da kara a kotu.
More Episodes
Published 05/08/19
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.
Published 04/17/19