Episodes
Published 05/08/19
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.
Published 04/17/19
Har yanzu Jam'iyyar APC ta gaza shawo kan matsalolinta da suka shafi 'yan majalisun da za su jagoranci majalisar Dattijai da ta wakilai, dai dai lokacin da ake ci gaba da fuskantar rarrabuwar kai.
Published 04/10/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan dambarwar zabukan Najeriya, in da Jam'iyyar adawa ta PDP ta garzaya kotu domin kalubalantar nasarar shugaba Muhammadu Buhari na APC a zaben 2019, yayinda ita ma APC a jihar Bauchi ta ruga zuwa kotu duk dai akan batun na zabe.
Published 03/20/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari ne game da zabukan Gwamnoni na 'yan majalisun jihohin Najeriya da za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa, in da ake fargabar cewa, da dama daga cikin Gwamnoni masu ci ba za su koma kan kujerunsu ba saboda wasu dalilai na siyasa.
Published 03/07/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne game da nasarar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu ta sake lashe kujerar shugabancin kasar wa'adi na biyu bayan doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar. Tuni Jam'iyyar PDP ta bayyana sakamakon zaben a matsayin mara inganci tana mai zargin tafka magudi a zaben,yayinda ta ce, za ta shigar da kara a kotu.
Published 02/28/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan mako da Bashir Ibrahim Idris ya gabatar, yayi nazari kan halin da siyasar Najeriya ke ciki, yayinda ya rage kwanaki kalilan a gudanar da zabukan kasar na 2019 a matakai daban daban. Sai kuma tsokaci da shirin ya yi kan yadda hankulan kasashen duniya ya karkata zuwa kan zabukan Najeriyar.
Published 02/13/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon, ya leka jihar Kano da ke tarayyar Najeriya, ida yayi nazari kan yadda al'amuran Siyasa ke gudana, yayinda ake gaf kada kuri'a a zaben shugabancin kasar na 2019 a ranar 16 ga watan Fabarairu.
Published 02/08/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan dambarwar siyasar da ta kunno kai a Najeriya bayan shugaban kasar Muhammadu Buhari ya dakatar da alkalin alkalai, Walter Onnoghen bisa zargin sa da bayar da bayanan karya kan kudaden da ya mallaka.
Published 01/31/19
Shirin Dandalin siyasa na wannan mako ya mayar da hankaline kan dakatar da babban mai shari'ar Najeriya Walter Onnonghen da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yayi.
Published 01/30/19
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan yadda 'yan siyasa ke ci gaba da sauya sheka a Najeriya a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben gama-gari a cikin watan gobe.
Published 01/17/19
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari da ya kaddamar da yakin neman zabensa a jihar Akwa Ibom, ya bayyana nasarorin da ya samu tun bayan darewarsa kan karagar mulki a shekarar 2015, in da yake cewa, gwamnatinsa ta murkushe mayakan Boko Haram duk da cewa kungiyar kan kaddamar da hare-hare jifa-jifa a yankin arewa maso gabashin kasar. Shugaban ya kuma bayyana irin nasarar da ya samu a fannin yaki da cin hanci da rashawa. Kuna iya latsa kan hoton don sauraren cikakken shirin kan yakin neman zaben...
Published 01/06/19
A wani taro da Tsohon Shugaban Najeriya Abdusalami Abubakar ya shirya,taron da ya hada yan siyasa da suka hada da Muhammadu Buhari shugaban kasar,wanda kuma ya sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin sa da sauran masu karawa da shi a zaben shekara mai zuwa. Wasu na bayyana cewa ba a gayyaci dan takara Atiku Abubakar a wannan taro,cikin shirin dandalin siyasa Bashir Ibrahim Idris ya samu tattaunawa da yan Najeriya.
Published 12/12/18
A cikin shirin dandalin Siyasa, Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali zuwa takaddama da ta kaure a yankin arewa maso gabacin Najeriya. Datijen wannan yankin sun bukaci a goyawa daya daga cikin yan takara a zaben Shugabancin kasar baya,labarin da wasu suka musanta. Bashir Ibrahim Idris ya samu zantawa da wasu daga cikin datijen yankin a cikin shirin  Dandalin siyasa daga nan Rfi.
Published 11/28/18
A cikin shirin dandalin siyasa,Bashir Ibrahim Idris ya samu tattaunawa da wasu mata dangane da rashin samun mata a fagen siyasar Najeriya,wasu daga cikin yan kasar mata musaman sun bayyana aniyar su ta kasancewa daga cikin yan takara a zaben shekarar 2019.
Published 11/14/18
Sashen Hausa na RFI na farin cikin gabatar muku da sabon shirin Dandalin Siyasa da zai rika nazari game da al'amuran da suka shafi siyasar Najeriya, Nijar, Afrika da sauran kasashen duniya. Shirin na makon farko tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari ne game da tasirin na'urar tantance masu kada kuri'u a zaben Najeriya, abin da masana ke cewa, ta na taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar magudi.
Published 11/08/18
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game da batun yin watsi da amincewa da jekadu 46 da Majalisar Dattiajan Najeirya ta yi da rikicin shugabannin Jamiyyar PDP mai adawa a Najeriya da ta dare gida biyu inda wasu ‘yan jam’iyyar ke neman a raba-gari wasu kuma ke bukatar sake lale.
Published 11/19/16
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game da batun yin watsi da amincewa da jekadu 46 da Majalisar Dattiajan Najeirya ta yi da rikicin shugabannin Jamiyyar PDP mai adawa a Najeriya da ta dare gida biyu inda wasu ‘yan jam’iyyar ke neman a raba-gari wasu kuma ke bukatar sake lale.
Published 11/19/16
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game sakamakon zaben Amurka inda masana suka yi sharhi akan nasarar da Donald Trump dan takarar Republican ya samu bayan ya doke abokiyar takararsa Hillary Clinton ta Democrat.
Published 11/14/16
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game sakamakon zaben Amurka inda masana suka yi sharhi akan nasarar da Donald Trump dan takarar Republican ya samu bayan ya doke abokiyar takararsa Hillary Clinton ta Democrat.
Published 11/13/16
Shirin Dandalin Siyasa ya yi nazari ne game da 'Yan takarar shugabancin Amurka guda biyu Donald Trump na Republican da Hillary Clinton da Democrat tare da tattauna manufofinsu. Sannan shirin ya yi tsokaci akan tasirin zaben Amurka ga Afrika.
Published 11/08/16
Shirin Dandalin Siyasa ya yi nazari ne game da 'Yan takarar shugabancin Amurka guda biyu Donald Trump na Republican da Hillary Clinton da Democrat tare da tattauna manufofinsu. Sannan shirin ya yi tsokaci akan tasirin zaben Amurka ga Afrika.
Published 11/06/16