Dandalin Siyasa - Kun san abin da Buhari ya fada a Akwa Ibom?
Listen now
Description
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari da ya kaddamar da yakin neman zabensa a jihar Akwa Ibom, ya bayyana nasarorin da ya samu tun bayan darewarsa kan karagar mulki a shekarar 2015, in da yake cewa, gwamnatinsa ta murkushe mayakan Boko Haram duk da cewa kungiyar kan kaddamar da hare-hare jifa-jifa a yankin arewa maso gabashin kasar. Shugaban ya kuma bayyana irin nasarar da ya samu a fannin yaki da cin hanci da rashawa. Kuna iya latsa kan hoton don sauraren cikakken shirin kan yakin neman zaben Buhari a Akwa Ibom.
More Episodes
Published 05/08/19
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.
Published 04/17/19