Description
Shirin Kasuwa Akai Miki Dole a wannan mako tare da Ahmed Abba ya yada zango ne a tarayyar Najeriya, inda mahawara ta kaure a kasar tun bayan matakin kara kudin Litar man fetir dana lantarki, inda a hannu guda kuma jama’a a sassan kasar ke cigaba da maida martani, lura da halin matsin rayuwar da aka tsinci kai sakamakon annobar corona, kuma sai gashi kwatsam an wayi gari da wannan yanayi, wanda galibin al ummar Najeriyar musamman talakawa, ke ganin zai sake jefasu su ne cikin mawuyacin hali kari kan wanda suke ciki.