Episodes
A wannan makon shirin zai yi duba kan cutar kyanda ko kuma measles a turance, cutar da galibi akan ga bullarta a irin wannan lokaci da ake fama da matsanancin zafi musamman a yankunan kasashen yammacin Afrika Sahel.
Published 05/13/24
Published 05/13/24
Shirin lafiya jari ce na wannan mako ya mayar da hankali ne kan tsarin yin kaho a zamanance
Published 05/06/24
Shirin Lafiya jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan makon ya mayar da hankali ne kan yadda al’ummar yankin arewacin kamaru ke fuskanta matsalar rashin tsaftatacce kuma wadataccen ruwan sha ba, wanda ke haddasa gagarumar matsala ga lafiyar mazauna yankunan, wannan shi ne maudu’in da shirin na wannan mako zai mayar da hankali akai.
Published 05/03/24
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne game da alfanun Azumi ga lafiyar jikin dan Adam. Masana kiwon lafiyar dai na bayyana cewar Azumi na taimakawa wajen rage kaifin wasu cutuka a jikin dan adam.
Published 04/01/24
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne kan irin cutukan da ke karuwa a lokutan Azumi musamman yadda a wannan karon ake gudanar da ibadar a cikin yanayi na tsananin zafi, wanda masana ke ganin akwai wasu naukan cutukan da ka iya bijorowa. Masana kiwon lafiya dai sun gargadi masu dauke da wasu nau'ukan cutuka kan irin matakan da ya kamata su dauka don kula da lafiyarsu.
Published 03/25/24
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne kan yadda aka gudanar da gangamin rigakafin cutar shan inna wato Polio a Jamhuriyar Kamaru don dakile bazuwarta. A baya-bayan nan ne dai ake ganin bullatar cutar a wasu sassan kasar, lamarin da ya sanya mahukunta tashi tsaye don yin rigakafin cutar.
Published 03/18/24
A wannan mako shirin ya mayar da hankali kan nau’ikan cutakan da ba a fiya mayar da hankali wajen yakarsu ba musamman a kasashe masu tasowa irin Najeriya, wannan nau’in cutuka kuwa sun kunshi kansar mafitsara ko kuma Prostate Cancer, nau’in kansar da ke matsayin mafi hadari ga maza, amma kuma ba ta samun kula duk da yadda ta ke kisan akalla mutum dubu 8 duk shekara a Najeriya. 
Published 03/04/24
Shirin Lafiya Jari ce a wannan karo ya mayar da hankali ne kan cutar cizon mahaukacin kare ko kuma Rabies a turance, bayan da bincike ya nuna cewar cutar na karuwa a Najeriya duk da cewa babu cikakkun alkaluman wadanda cutar ta shafa saboda karancin kawo rahoton cutar ga mahukunta.
Published 02/26/24
A wannan makon shirin Lafiya Jari ce ya mayar da hankali ne kan cutar kazuwa ko kuma Smallpox a turance, cutar da ke sahun cutuka masu matukar hadari da ke haddasa kuraje masu matukar kaikayi da mashasshara da kuma hana barci, wadda Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta sanar da kawar da ita daga ban kasa tun a shekarar 1980 amma kuma duk da haka ake ganin bullarta lokaci zuwa lokaci.
Published 02/19/24
A wannan makon shirin ya mayar da hankali kan yawaitar gurbatattun jami’an lafiya a asibitocin Najeriya wanda ke da nasaba da kodai rashin samun cikakken horo a kwalejojin lafiya ko kuma samun horon irin wadannan makarantu amma na bogi. A baya-bayan nan ana yawan ganin yadda ake bude tarin makarantu masu zaman kansu a sassan Najeriya da sunan horar da jami’an lafiya kama daga kwalejoji har da jami’o’I wadanda wasu daga cikinsu kan rasa sahalewar mahukuntan saboda rashin cancanta.
Published 01/29/24
Shirin Lafiya Jari ce tare da Azima Bashir Aminu a wannan makon ya yi duba ne kan illar dafin miciji ga lafiyar bil'adama dai dai lokacin da asibiti daya tilo da ke lura da wadanda suka gamu da cizon na maciji ke ganin koma baya.
Published 01/22/24
A wannan mako shirin ya mayar da hankali ne kan ci gaban da aka samu na fara amfani da fasahar fida ba tare da tsaga jikin majinyaci ba a Najeriya, a wani yunkuri na rage dogaro da kasashen ketare wajen irin wannan fida.  
Published 12/18/23
Shirin 'Lafiya Jari Ce' na wanna makon tare da Murtala Adamu Ibarhim ya maida hankali ne kan shirin gwamnatin Najeriya na sake daukar likitoci da sauran jami'an kiwon lafiya wadanda suka yi ritaya daga aiki, a wani kokari na cike gibin karancin jami'an kiwon lafiya a kasar, masamman guraben wadanda suka tsere zuwa kasashen waje domin samun albashi mai soka.
Published 11/13/23
Shirin Lafiya Jari Ce na wannan makon ya tattauna ne kan musabbabin kamuwa da ciwon koda a daidai lokacin da wasu alkaluma ke nuni da cewa, akwai mutane kimanin miliyan 17 da ke fama da cutar a Najeriya.
Published 10/26/23
Shirin Lafiya Jari Ce na wannan makon ya tattauna ne kan musabbabin kamuwa da ciwon koda a daidai lokacin da wasu alkaluma ke nuni da cewa, akwai matasa kimanin miliyan 5 da ke fama da ciwon koda a kasar Ghana.
Published 10/26/23
Shirin a wannan mako ya yi duba kan karuwar masu kamuwa da cutar kansa ko kuma Sankara koma Daji kamar yadda hausawa ke kira, cutar da a bara kadai Najeriya ta samu sabbin kamuwa akalla dubu 131 baya ga wasu dubu 78 da cutar ta kashe. 
Published 10/09/23
Shirin 'Lafiya Jari Ce' na wannan makon ya tattauna da masana akan matsalar ciwon idanu na Apollo da a baya bayan nan ya sake bulla a sassan Najeriya.
Published 10/02/23
Shirin 'Lafiya Jari Ce'  na wannan mako ya yi nazari ne kan hanyoyin gargajiya da ake bi wajen magance cutar  sikila  da kuma yadda al'umma suka karbi wadannan hanyoyi don samar wa kansu mafita. Shirin ya tattauna da masu maganin gargajiya da ke ikirarin cewa magungunansu na samar da waraka, kana ya gana da  liitocin zamani don neman karin haske a kan inda aka kwana wajen neman mafita a game da wannan cuta ta sikila. 
Published 09/18/23
Shirin Lafiya Jari na wannan mako ya duba irin nasarorin da ake samu ta fannin yiwa matan da suka kasa daukar ciki dashen cikin a kimiyyance.
Published 09/11/23
Shirin lafiya jarice na wannan mako, ya duba irin kalubalen da mata ke fuskanta a yayin daukar ciki, haihuwa da kuma rainon jarirai.
Published 09/04/23
Shirin Lafiya Jari ce a wannan makon tare da Azima Bashir Aminu ya mayar da hankali kan wani gangamin gwajin cutar kansar mama da ta bakin mahaifa da mahukuntan Nijar suka gudanar a jihar Maradi a wani yunkuri na lalubo masu cutar tare da yi musu magani.
Published 08/28/23
Shirin Lafiya Jari a wannan makon zai yi duba ne kan binciken wata cibiyar bin diddigi kan harkokin kiwon lafiya ta Nigeria Health Watch wanda ya nuna cewa mace daya cikin masu juna biyu 95 na mutuwa a lokacin haihuwa a jihar Neja ta arewacin kasar, lamarin da ake ganin akwai sakaci na al'umma da kuma rashin kulawar hukumomin kula da lafiya a jihar ta fannin samar da kwararrun ma'aikata a dukkanin asibitocin jihar.  
Published 08/21/23
daruruwan dubban mutane ne ke mutuwa sanadiyar kwankwadar gurbatacen magani a duniya, al'amarin dake ci gaba da saka ciwon kai, ga mahukumta dake ta kokarin ganin sun magance matsalar bazuwa magungunnan jabu a duniya, a kan haka cikin shirin Azima Bashir Aminu ta duba mana yadda matsalar ta yi kamari a kasar Kamaru.
Published 08/14/23
Shrin 'Lafiya Jari Ce' na wannan mako zai mayar da hankali ne a kan cutar rashin bacci, ko kuma rashin samun baccin a lokacin da ake bukata.  Alkalumma sun nuna cewa kashin 30 zuwa 35 na al'ummar duniya, wadanda shekarunsu ya kai 18 zuwa sama na fama da wannan cuta ta rashin samun isassehn bacci wadda ake kira insomnia a turance. Shirin ya tattauna da kwararren likita, wanda ya yi bayani a game da wannan cuta da ta addabi al'umma.. 
Published 07/31/23